Yan bindiga sun sace ɗaliban firamare 6 a jihar Nasarawa

Yan bindiga sun sace yara 6 a firamaren LEA dake Alwaza a ƙaramar hukumar Doma ta jihar Nasarawa.

Rahotanni sun bayyana cewa yan bindigar sun sace yaran ne da misalin ƙarfe 07:00 na safe.

Rahman Nansel kakakin rundunar yan sandan jihar Nasarawa shi ne ya tabbatar wa da jaridar The Cable faruwar lamarin.

Nansel ya kara da cewa tuni aka bincike tare kokarin ceto yaran.

Jihar Nasarawa dai na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya dake fama da matsalolin tsaro.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...