Wasu ‘yan bindiga sun kai hari da tsakar dare a arewa maso gabashin Burkina Faso, kuma farar hula 20 ne suka mutu.
‘Yan bindigar da sun kai harin a daren Asabar akan babura dauke da muggan makamai, sun afkawa kauyen Bani, da ke arewacin birnin Ouagadougou, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayyana.
Wannan hari na zuwa ne mako guda da ‘yan bindiga suka kai hari kasuwar Silgadji da ke yankin, tare da hallaka mutane 39.
Yankin Sahel dai na fama da hare-harenb ‘yan bindiga da mayakan jihadi a dan tsakanin nan.
Bayanan harin ranar Asabar na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Faransa ta sanar da tura karin dakaru 600 yankin Sahel, wanda hakan ya kai adadin sojojin kasar a yankin 5,000 dan tabbatar da zaman lafiya da yakar mayakan jihadi.
A shekarar da ta gabata yankin ya fuskanci kashe-kashen mutane sama da 4,000 daga mayakan jihadi, wanda aka dade ba a ga irinsa ba tun shekarar 2011.