Yan bindiga sun kashe fasinjoji biyar tare da  yin garkuwa da wasu 14 a jihar Kogi

Mutane biyar aka bada rahoton an kashe a yayin da aka yi garkuwa da wasu da dama a wani farmaki da wasu yan bindiga su ka kai kan wata motar fasinja a kusa da wani shingen binciken sojoji a jihar Kogi.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya rawaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:10  na daren ranar Juma’a a a dai-dai lokacin da wasu batagari dake dauke da makamai suka bude wuta kan motoci dake tsaka da tafiya akan titin Oshokoshoko/Agbede.

A cewar rahoton  lamarin ya rutsa da wata mota kirar Toyota Hummer mai É—auke da rijistar nambar jihar Jigawa HJA 687 YD  dauke da fasinjoji daga Abuja zuwa garin Ilesha na jihar Osun.

“Gawarwaki biyar da ba a san ko su waye ba aka gano a wurin da abun ya faru” a cewar wata majiya.

Majiyar  ta kara da cewa an samu nasarar ceto daya daga cikin fasinjojin mai suna  Naziru Aliyu wanda ya samu raunin harbin bindiga inda aka garzaya da da shi Asibitin Fisayo  a yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawarwaki na Asibitin Koyarwa na Tarayya dake  Lokoja.

Rahoton ya kara da cewa DPO yan sanda na Obajana tare da sauran jami’an tsaro sun isa  wurin inda suka fara aikin kuÉ“utar da sauran mutanen.

Bayan bincike a cikin janina sun samu nasarar kuɓutar da wasu fasinjoji 14 da aka yi garkuwar da su.

More from this stream

Recomended