Wasu ’yan bindiga da ake zargin Lakurawa ne sun kai hari cikin wani masallaci da ke garin Dadinkowa, a Ƙaramar Hukumar Maiyama ta Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyar tare da jikkata wasu biyar yayin da ake tsaka da sallah.
Wani mazaunin yankin da gidansa ke kusa da masallacin ya bayyana cewa maharan sun shigo garin a ɓoye a daren Laraba, bayan sun kashe fitilun baburansu. Ya ce sun leƙa cikin masallacin suka ga mutane na ibada ba tare da makami ba, sai suka buɗe musu wuta.
“Nan take suka kashe mutum biyar, wasu biyar kuma suka jikkata. An kai waɗanda suka ji rauni asibiti,” in ji shi.
Shaidar ta kuma ce da zarar an fara jin ƙarar harbe-harbe, jama’a suka rika gudu domin tsira da rayukansu, yayin da maharan suka ci gaba da harbi a iska kafin su fice daga garin.
An kuma bayyana cewa maharan ba su yi yunƙurin yin garkuwa da kowa ba, lamarin da ke nuna cewa harin na iya kasancewa ramuwar gayya kan wasu hare-haren da aka ce sojoji sun kai musu a yankin.
Bayan aukuwar lamarin, jami’an tsaro ciki har da sojoji da ’yan sanda sun isa yankin domin tabbatar da zaman lafiya, yayin da kakakin ’yan sandan jihar bai samu damar yin karin bayani kan lamarin ba.
’Yan Bindiga a Jihar Kebbi Sun Kqshe Mutum 5 A Masallaci

