
Asalin hoton, AFP
Iyalan ‘yan sandan sun yi kira da a ceto mazajensu
Iyalan wasu manyan jami’an ‘yan sanda su goma sha biyu da ‘yan bindiga suka sace suka kuma yi garkuwa da su a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa jihar Zamfara daga jihar Borno, sun shiga cikin damuwa game da makomar mazajen nasu tun bayan da aka sace su.
Kwanaki goma da suka gabata ne ‘yan bindigar suka sace manyan jami’an ‘yan sandan masu mukamin ASP a wani kauye da ke tsakanin jihohin Katsina da Zamfara amma sai yanzu labarin satar tasu ya fito.
Iyalan ‘yan sandan sun shaida wa BBC cewa suna kan hanyarsu ne daga jihar Borno domin zuwa gudanar da wani aiki na musamman a jihar ta Zamfara sai kawai ‘yan bindiga suka yi musu kwanton-bauna inda suka kama su.
Matar daya daga cikin ‘yan sandan ta shaida wa BBC cewa kwana uku ba ta ji labarin mijinta ba sai da ta je barikin ‘yan sandana na jihar Borno ne ta samu labarin cewa an sace mazajen nasu, kuma daga bisani ta ce biyu sun tsere daga hannu ‘yan bindigar inda suka buga waya helkwata cewa an tafi da sauran.
Ta kara da cewa ce daga bisani ta samu magana ta waya da maigidan nata amma a takaitacccen lokaci, inda ya bayyana mata halin da suke cikin a hannun masu garkuwa da su.
“A ranar Laraba ne ya bugo ya ce min sun shiga hannun masu garkuwa da mutane, ya ce don Allah a yi kokari a jinginar da gidansa a samu ko da naira miliyan daya ne a gaggauta idan ba haka ba za a samu matsala,” in ji ta.
Ta ce tun daga ranar ba ta sake jin muryarsa amma wani a cikin jami’an ‘yan sandan ya buga mata waya inda ya ce mata su gaggauta harhada kudaden fansar tasu gabaki daya.
A cewarta: “Ya ce za a harhada dubu dari takwas-takwas kowannensu, muna kokarin hadawa – ga mu nan dai ba ma iya barci sai addu’ar Allah ya fitar mana da su lafiya.”
Matar ta bayyana cewa mai dakin daya daga cikin ‘yan sandan da ke hannun masu garkuwa da mutanen ta rasu ta bar ta bar masa ‘yaya biyar da yanzu haka suna barikin ‘yan sanda a jihar Borno.
“Ba zan iya ce maka ina da wani sauran bayani ba, mu dai ga shi nan muna cikin takaici, Allah ya fito mana da su lafiya, a yi mana kokari don Allah a fito mana da su, ga ‘ya’ya nan ba wanda suka mallaki aikin kansu, addu’ar da muke yi shi ne Allah ya fito mana da mazajenmu,” a cewar matar.
BBC ta tuntubi masu magana da yawun ‘yan sandan jihohin Zamfara da Katsina, inda ake tunanin lamarin ya faru, amma sun ce ba su da masaniya kan sace jami’an nasu.
Sai dai iyalan wadannan jami’an ‘yan sandan na ci gaba da kiran da a kai wa mazajen nasu dauki a hannun ‘yan bindigar da suka yi garkuwa da su.
Satar mutane domin karbar kudin fansa ta zama ruwan dare a arewa maso yammacin Najeriya musamman a jihohin Zamfara da Katsina.
Hukumomi sun ce suna daukar matakan kare al’umma daga wadannan masu satar mutane amma mazauna yankunan sun ce har yanzu ba su gani a kasa ba.