‘Yadda na jefar da dana saboda na haife shi ba bisa sunna ba’

[ad_1]

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Hira da wacce ta taba jefar da danta

Ku latsa alamar lasifikar da ke sama don sauraron cikakkiyar hirar Halima Umar Saleh da Hariya wacce aka sauya muryarta.

A tsarin rayuwar Bahaushe, babu wani abu da ya fi takaici da kunya irin a ce mace ta yi ciki ba tare da aure ba.

Hakan ce ta sa idan har irin wannan kaddara ta fada wa wasu, sai su yi duk kokarin da za su yi don gujewa haifar cikin.

Halima Umar Saleh, ta ci karo da wata baiwar Allah a birnin Kano, wacce ta fayyace mata labarin wani al’amari da ya faru da ita shekara 12 da suka gabata, na yadda ta yi ciki ba aure ta kuma haifi dan, amma saboda gudun abin kunya sai ta dauki wani mataki da ya sa ta da-na-sani tun ba a je ko ina ba.

Wannan baiwar Allah da muka boye sunanta na gaskiya muka sa mata suna Hariya, ta ce ta tsinci kanta a wani mummunan yanayi yayin da aka wayi gari ta ganta dauke da ciki ba tare da ta yi aure ba.

Hariya mai shekara 35 ta ce tana da shekara 23 ne wani mutum ya yaudare ta ya yi mata ciki, kuma daga baya ya kekasa kasa ya ce cikin ba nasa ba ne.

“Lokacin da na samu cikin na sha wahalar da ban taba tsammanin zan rayu ba, iyayena suka kore ni, sai na koma gidan yayar mahaifina na zauna a can har na haihu.

“Manyana sun so a zubar da cikin don har mun je asibiti, amma sai aka ce ina iya rasa raina sakamakon haka. Wannan tsoron ne ya sa na ce gaskiya abar min cikin kawai.”

Yaya aka yi da dan?

Hariya ta ce bayan kwanaki kadan da haihuwarsa sai ta faki idon mutane ta kai shi kofar wani gida ta ajiye shi, ta juya ta tafi.

“Amma da na koma gida sai tunani da damuwa suka shige ni, sai na shaida wa yayar mahaifina cewa na kai yaron nan wani gida amma kuma yanzu na kasa samun nutsuwa.

“Sai muka je don dauko yaron, sai muka samu har an yi cincirindo ana ta ganin dan da kuma jimamin yadda aka jefar da shi,” in ji Hariya.

Ta ci gaba da cewa: “Da kyar suka yarda suka ba mu dan bayan sun ja min kunne kan rashin kamatar abun da na yi.”

Rashin aure

Duk da cewa Hariya ta yi da-na sanin abun da ta yi, amma har yanzu shekara 12 bayan hakan ba ta yi aure ba.

Ta alakanta hakan da yadda ake kyamar auren duk wacce ta taba haifar dan da ba na sunna ba a kasar Hausa, duk kuwa da tarin nadamarta.

Sai dai ta ce ita wannan ba ya damunta, a yanzu burinta shi ne ta yi wa danta kyakkyawar tarbiyya ta kuma taimaka wajen ba shi ilimi ta yadda rayuwarsa ba za ta tagayyara ba.

[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...