Yadda mata ke karuwanci don burge mutane a Kenya

[ad_1]

Mata na karuwanci don birge mutane a kafafan sada zumunta a Kenya

Mata matasa na amfani da maza ‘yan daduro wajen samun kudaden da za su yi rayuwa don burge mutane a kafafan sada zumunta a kasar Kenya.

Wata mai shirya fina-finai, Nyasha Kadandara, ta ce mata na amfani da karuwanci wajen kawar da talauci, amma kuma a yanzu ya zamo abin burgewa.

BBC ta gudanar da bincike a kan wasu mata uku.

Ta farko mai buge-buge ce, sunanta Kal, mace ce mai da amma kuma ba ta da miji kuma tana rawa a gidajen rawa musamman da daddare, sannan babban burinta shi ne ta zamo tauraruwa.

Ta je Kenya in da ta nemi mai kudin da zai dauki nauyinta wato daduron da zai cika mata burinta ta zama mawakiya.

To amma kuna ganin wannan hanya ce mai sauki da mutum zai samu kudi?

Mace ta biyu daliba ce.

Yawanci dalibai a birnin Nairobi sun fi son yin soyayya da tsofaffi maza maimakon daidai su.

Jane ‘yar shekara 21 ce kuma daliba ce, koda yake ta fito ne daga wani kauye wadanda suke daraja al’ada.

Ta ce ta na samu taimakon karatunta ne daga wajen wasu daduronta tsofaffi guda biyu.

Mace ta uku Bridget Achieng, mai tallan kayan kawa ce kuma ta shahara a wasu shirye-shirye da ake nuna wa a gidan talabijin.

Ta ce ta samu wannan rayuwa ne ta hanyar kwanciya da manyan masu hannu da shuni.

[ad_2]

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...