‘Yadda hotunan tsiraici suka tagayyara rayuwa ta’ | BBC Hausa

Tutar Zimbabwe

Hakkin mallakar hoto
ZINYANGE AUNTONY

Image caption

Gwamnatin Zimbabwe na kokarin gabatar da kudurin doka da zai bai wa matan da aka ci zarfinsu ta internet kariya

Cin zarafi a shafukan sada zumunta da ramuwar gayya ba boyayyen abu ba ne idan ana maganar cin zarafin jinsi da wadanda abin ya shafa a kasar Zimbabwe, domin haka na fara tashi da yaki da mummunar dabi’ar.

Mata biyu da shirin BBC She Word ya zanta da su sun bayyana yadda wasu bidiyon badala da aka yada dan ramuwar gayya suka daidaita rayuwarsu, ciki har da dakatar da zuwa makaranta da kora daga wurin aiki.

Daya daga cikin matan da ba za mu bayyana sunanta ba, ta bayyana yadda saurayinta ya wallafa hotonta tsirara a shafin internet bayan sun samu sabanin da ya raba su.

”Ya turo mani sakon wayar salula inda ya ce: ‘Kin san ina da wadannan hotunan, ‘Sai na ce wa kai na; ‘Ba zai yi mani haka ba.”

”Bayan kwana biyu, na tashi daga bacci na ga yadda sakonni ke shigowa cikin waya ta. Kawayena, kawunnina, goggonnina da abokan arziki sai kira na suke yi ta waya, ana ta maganganun da ba na fahimta kamar na fara zarewa.

“Sai wata kawata ta turo mani da hotunan, a lokacin da na kalla abin da na fara rayawa a zuciyata shi ne: “Kai wannan ba ni ba ce, ba zai yi mani haka ba,” sai da numfashina ya dauke na wani lokaci,” inji ta.

  • Yadda wata ‘yar Indiya ke amfani da tsiraici don nema wa mata ‘yanci
  • An hana mata bayyana tsiraici da karin gashi a ofisoshi a Uganda

Matsalar ita ce, tana rayuwa tare da saurayin da ya ci zarafinta ba tare da sanin ‘yan uwanta ba, bayyanar hotunan ta sanya ta shiga taskun rayuwa.

”Ban isa na fita daga gida ba, ba na iya magana da kowa. Kullum ina kunshe a dakina, kawunnina da goggonina sun tsine mani sun ce babu ruwansu da ni.”

”Ya kamata a ce sun biya mani kudin makaranta, amma su suka yanke shawarar ba zan koma makaranta ba.

“Daya daga cikin kawunnina cewa ya yi; “Tun da kin yanke shawarar fara sana’ar daukar hotunan tsiraici, to ki mayar da hankali a kai babu zancen zuwa wata makaranta,” haka ta shaida wa shirin BBC She Word.

Fitacciyar mai gabatar da shiri a gidan rediyon Zimbabwe Tino Katsande ta taba daukar bidiyon badala ita da tsohon saurayinta, budurwarsa ce ta yada shi a internet.

”Lamarin da dare ya faru, na tashi daga mai farin jini zuwa mujiya. Mako uku bayan bullar bidiyon aka kore ni daga wurin aiki,” inji Katsande.

Tun daga wannan lokaci ne Mis Katsande ta kafa wata kungiya mai suna Speak Out Handinyarare, wadda ke bai wa matan da aka ci zarafin su ta irin wannan hanyar damar bayyana halin da suka samu kan su a ciki da kuma ba su kariya.

A halin da ake ciki dai gwamnatin Zimbabwe na kokarin gabatar da kudurin doka da zai bai wa matan da aka ci zarfain su ta internet kariya.

More from this stream

Recomended