Yadda ake cinikin ragunan Sallah a Intanet a Algeria

[ad_1]

Ana sayen miliyoyan raguna da tumaki domin Sallar layya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Ana sayen miliyoyan raguna da tumaki domin Sallar layya

Matsalar satar ragunan Sallah ya sa masu sayar ragunan Sallah da tumaki a Algeria sun koma suna amfani da shafin Facebook da wasu shafukan intanet domin tallar dabbobinsu.

Suna fatan cinikayya ta hanyar Intanet zai kare su daga hatsarin da ke tattare da daukar dabbobinsu zuwa birane don sayar wa a lokuttan sallar layya, saboda an dade ana yi wa ‘yan kasuwa duka a kwace dabbobinsu, kamar yadda shafin labarai na Echouurouk ya ruwaito.

Shafin Facebook da Ouedkniss.com a Algeria, ya ba ‘yan kasuwa damar saka hutunan dabbobinsu daga gida domin talla.

Sannan akwai wani shafi kuma da ke tallar dakon dabbobin ga ‘yan kasuwa zuwa ga wadanda suka saya a Intanet.

‘Yan kasuwar yanzu na amfani da shafin Facebook domin tallar ragunan sallah a sassan Algeria don gujewa hatsarin da ke tattare wajen kwasar ragunan zuwa birane domin sayar wa ga masu bukatar yin layya.

Hakkin mallakar hoto
Ouedkniss.com

Image caption

‘Yadda ake tallar Raguna da Tumaki a Intanet.

Ana sa ran za a yi layya da dabbobi kusan miliyan shida a Algeria a bana, sabanin miliyan hudu da aka yanka a shekarun baya.

Kungiyar manoma ta Algeria ta ce tana son sawwake wa mutane dabbobin layya inda za su iya saya cikin sauki.

A ranar 21 ga watan Agusta ake sa ran gudanar da sallar layya, biki na biyu mafi muhimmaci ga musulmi bayan bikin Sallar Azumi wato Eid el-fitr.

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...