Yadda ake cinikin ragunan Sallah a Intanet a Algeria

[ad_1]

Ana sayen miliyoyan raguna da tumaki domin Sallar layya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Ana sayen miliyoyan raguna da tumaki domin Sallar layya

Matsalar satar ragunan Sallah ya sa masu sayar ragunan Sallah da tumaki a Algeria sun koma suna amfani da shafin Facebook da wasu shafukan intanet domin tallar dabbobinsu.

Suna fatan cinikayya ta hanyar Intanet zai kare su daga hatsarin da ke tattare da daukar dabbobinsu zuwa birane don sayar wa a lokuttan sallar layya, saboda an dade ana yi wa ‘yan kasuwa duka a kwace dabbobinsu, kamar yadda shafin labarai na Echouurouk ya ruwaito.

Shafin Facebook da Ouedkniss.com a Algeria, ya ba ‘yan kasuwa damar saka hutunan dabbobinsu daga gida domin talla.

Sannan akwai wani shafi kuma da ke tallar dakon dabbobin ga ‘yan kasuwa zuwa ga wadanda suka saya a Intanet.

‘Yan kasuwar yanzu na amfani da shafin Facebook domin tallar ragunan sallah a sassan Algeria don gujewa hatsarin da ke tattare wajen kwasar ragunan zuwa birane domin sayar wa ga masu bukatar yin layya.

Hakkin mallakar hoto
Ouedkniss.com

Image caption

‘Yadda ake tallar Raguna da Tumaki a Intanet.

Ana sa ran za a yi layya da dabbobi kusan miliyan shida a Algeria a bana, sabanin miliyan hudu da aka yanka a shekarun baya.

Kungiyar manoma ta Algeria ta ce tana son sawwake wa mutane dabbobin layya inda za su iya saya cikin sauki.

A ranar 21 ga watan Agusta ake sa ran gudanar da sallar layya, biki na biyu mafi muhimmaci ga musulmi bayan bikin Sallar Azumi wato Eid el-fitr.

[ad_2]

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...