Yadda Ƙin Fitowar Masu Kaɗa Kuri’a, Sayen Kuri’u Da Tashin Hankali Suka Gurgunta Zaɓen Kananan Hukumomi A Abuja

Zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar a Babban Birnin Tarayya (FCT) ya fuskanci matsaloli da dama, inda rahotanni suka nuna ƙarancin fitowar masu jefa ƙuri’a, zargin sayen kuri’u da kuma tashin hankali a wasu wurare.

Rahotanni sun nuna cewa yawancin masu kaɗa ƙuri’a sun zauna a gida saboda rashin gamsuwa da tsarin siyasa da kuma rashin amincewa da yadda ake gudanar da zaɓe. A wurare da dama kamar Jikwoyi, Karu, Bwari, Gwagwalada, Nyanya, Mpape, Deidei, Kuje, Kwali, Lugbe da Durumi, an samu ƙarancin mahalarta zaɓen.

Haka kuma, jam’iyyun adawa sun soki yadda aka gudanar da zaɓen, inda suka ce babu gaskiya da riƙon amana. An kuma yi zargin cewa an riƙa sayen kuri’u a wasu yankuna, duk da gargadin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) da jami’an tsaro suka bayar.

Wasu wakilan jam’iyyun PDP da YPP sun bayyana cewa an ga wasu jiga-jigan jam’iyyar APC suna zagayawa wuraren zaɓe da kuɗi domin jawo hankalin masu jefa ƙuri’a. An ce ana sayen kuri’u daga Naira 500 zuwa Naira 3,000.

Bugu da ƙari, an samu tashin hankali a wasu wuraren zaɓe, musamman a Bwari, inda masu kaɗa ƙuri’a suka gudu bayan barkewar rikici. Wata mata, Mrs. Omeza, ta ce:

“They teargassed us, they didn’t want us to vote. People are crying, people that are fasting are being teargassed and harassed.

“They just managed to come out, all of them have gone back and they don’t want to come out anymore”.

A Kuje ma, wani jami’in DSS ya tsallake rijiya da baya bayan da wasu matasa suka kai masa hari, inda aka lalata wayarsa tare da sace walat dinsa.

Wasu mazauna yankin sun kuma zargi Ministan FCT, Nyesom Wike, da zuwa wuraren zaɓe domin tsoratar da ‘yan adawa. Wani ɗan jam’iyyar ADC ya ce:

“was moving from one polling unit to another to intimidate voters”.

“Why was he going to polling units all in the name of monitoring elections? Is he eligible? He is not an eligible voter so what is he doing in polling units?

“Anywhere he goes, you will see the APC supporters screaming and making all kinds of notices to intimate people that aren’t voting for them. This is not right.

“It was another campaign because wherever he goes, he talks to his supporters. This is not right but those who should act have been bought over”.

Har zuwa lokacin tattara wannan rahoto, ana jiran sanar da sakamakon ƙarshe na zaɓen.

More from this stream

Recomended