Wuta ta kama tashar jirgin ƙasa na zamani a Legas

Wuta ta tashi a kan wani ƙaramin yanki na layin Lagos Blue Line a wuri da ke fuskantar tashar NEPA, kusa da gadar Eko, a yankin Apogbon na Jihar Lagos.

A cewar wani rubutu da Gboyega Akosile, mai magana da yawun Gwamnan Jihar Lagos, Babajide Sanwo-Olu, ya wallafa a shafin sa na X.com @gboyegakosile, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:12 na yamma ranar Asabar.

Akosile ya kuma bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, sannan babu wani jirgin ƙasa da ke aiki a lokacin da abin ya faru.

Ya ƙara da cewa tawagar ƙwararrun ma’aikatan lafiya da masu aikin ceto, tare da sauran masu amsa kira na farko, sun kashe wutar gaba ɗaya.

More News

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da dokar kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da kudirin dokar da zai samar da hukumar  da za ta kula da da mutane masu buƙata ta...

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da dokar kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da kudirin dokar da zai samar da hukumar  da za ta kula da da mutane masu buƙata ta...

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da dokar kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

Majalisar dokokin jihar Gombe ta zartar da kudirin dokar da zai samar da hukumar  da za ta kula da da mutane masu buƙata ta...

Wani gini ya ruguzo kan mutane a Abuja

Mutane da dama ne suka makale a kasan ɓaraguzan wani gini da ya ruguzo a yankin Sabon Lugbe dake birnin tarayya Abuja. Wasu bayanai sun...