Wike Ba Memban APC Ba Ne Amma Yana Aiki Da Gwamnatin Tinubu – Ajibola

Sakataren Ƙasa na jam’iyyar APC, Ajibola Basiru, ya bayyana cewa Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ba memba na jam’iyyar ba ne, amma yana aiki ne tare da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Basiru ya yi wannan bayani ne a wata hira da ya yi a shirin talabijin na Beyond The Headlines, inda ya ce duk da cewa Wike ba ɗan APC ba ne, yana gudanar da aikinsa ƙarƙashin gwamnatin tarayya da jam’iyyar ke jagoranta.

Ya ce irin ci gaban ababen more rayuwa da aka samu a FCT cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata ya taimaka matuƙa wajen nasarar APC a zaɓukan ƙananan hukumomi na yankin.

A cewarsa, an samu gagarumin ci gaba ba kawai a birane ba har ma da yankunan bayan gari, inda ya bayyana aikin ministan da cewa “sterling.”

Basiru ya ƙara da cewa haɗin gwiwar jam’iyyar da kuma zaɓen ’yan takara masu ingantaccen tarihi a siyasa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar APC a zaɓen.

More from this stream

Recomended