Wata mata mai suna Fatima Alaramma ta daɓa wa yarinya ‘yar shekara bakwai mai suna Sharifa Usman wuka a ciki, inda ta zargi mahaifinta da baiwa mijinta shawarar ya auri mata ta biyu.
Fatima ta jefar da yarinyar ne bayan ta daba mata wuka a wani gini da ba a kammala ba a Mariri, unguwar Hotoro a Kumbotso a cikin birnin Kano.
An ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne a unguwar Gadon Kaya da ke Gwale a cikin birnin Kano.
Wadanda suka ga lamarin sun shaida cewa matar wadda a halin yanzu ta gudu ta yanke shawarar daukar fansa kan diyar mutumin da yanzu haka take jinya a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH).