Wata ta caka wa yarinya wuƙa saboda mahaifinta ya shawarci mijinta ya mata kishiya

Wata mata mai suna Fatima Alaramma ta daɓa wa yarinya ‘yar shekara bakwai mai suna Sharifa Usman wuka a ciki, inda ta zargi mahaifinta da baiwa mijinta shawarar ya auri mata ta biyu.

Fatima ta jefar da yarinyar ne bayan ta daba mata wuka a wani gini da ba a kammala ba a Mariri, unguwar Hotoro a Kumbotso a cikin birnin Kano.

An ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne a unguwar Gadon Kaya da ke Gwale a cikin birnin Kano.

Wadanda suka ga lamarin sun shaida cewa matar wadda a halin yanzu ta gudu ta yanke shawarar daukar fansa kan diyar mutumin da yanzu haka take jinya a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

More from this stream

Recomended