Wata mata ta yi garkuwa da ƴarta a Kano

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta yi nasarar damƙe wata mata mai suna Rahama Sulaiman da zargin yin garkuwa da ƴar da ta haifa.

Rahotannin da muka sun nuna cewa Rahama dai tana neman kuɗin fansa har naira miliyan uku.

A cewar ƴan sandan, sun samu rahoto daga mijin matar, Kabiru Shehu Sharaɗa, kan cewa, Rahama Sulaiman mai shekaru 25, ta sanar da shi ƴarsa Hafsat Kabiru mai shekaru 6 ta ɓata ba a gan ta ba.

Bayan gudanar da bincike sai aka gano cewa Rahama Sulaiman ta ɓoye yarinyar ne, a Madobi, domin yin amfani da wannan damar don neman kuɗin fansa.

Ƴan sanda sun kamo ta, domin ci gaba da bincike, sai dai rahotanni na nuni da cewa, mijin matar ya mayar da ita gidansa tun a wajen ‘yan sandan, bayan sakin da ya yi.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...