Wata mata ta kashe masoyinta da kwalba

Wata mata yar shekaru 26 mai suna, Gift Obieriei, ta cakawa masoyinta wuka mai suna, Eghosa Iguodala har ta kai ya rigamu gidan gaskiya a Benin babban birnin jihar Edo.

Jaridar Dailly Trust ta rawaito cewa tuni jami’an yan sanda suka yi awon gaba da matar wacce ta fito ne daga karamar hukumar Ethiope East a jihar Delta.

Wata majiya ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Litinin inda matar ta cakawa masoyin nata fasasshiyar kwalba.

Lamarin ya faru ne bayan da masoyin ya bita da adda biyo ganinta da yayi ta ziyarci gidan wani namiji.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Edo, SP Chidi Nwabuzor ya tabbatar da faruwar lamarin.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...