Wata Mata Ta Gudu Bayan Ta Yanki Mijinta da Wuƙa a Mazaƙuta

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta tabbatar da faruwar wani rikicin cikin gida da ya jikkata wani magidanci a garin Potiskum.

Rahotanni sun ce wata matar aure mai shekara 18, Khadija Jamilu, ta kai wa mijinta mai shekara 25 hari da wuka, inda ta yi masa mummunan rauni a al’aurarsa.

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a cikin garin Potiskum.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, inda ya ce matar na hannun gudu har yanzu.

“Following the report, police operatives promptly visited the scene and rushed the victim to the State Specialist Hospital, Potiskum, for urgent medical attention.

“He was subsequently referred to the Federal Medical Centre (FMC), Azare, where he is currently receiving treatment”, in ji SP Abdulkarim.

Ya kara da cewa jami’an tsaro na ci gaba da kokarin cafke wadda ake zargin, yayin da bincike kan lamarin ke gudana.

A cikin sanarwar, Kwamishinan ’yan sandan Jihar Yobe, Emmanuel Ado, ya yi Allah-wadai da harin, yana mai jaddada cewa aure ya kamata ya ginu a kan mutunta juna, fahimta, hakuri da juriya.

Haka kuma ya ce bai kamata aure ya zama hanyar cin zarafi, tashin hankali ko wulakanci ba.

More from this stream

Recomended