Wata Jami’a Ta Dakatar Da Ma’aikacinta Bisa Zargin Neman Lalata Da Ɗaliba

Jami’ar Clifford da ke Owerrinta, Jihar Abia, ta dakatar da wani jami’in ta mai suna Mista Obioma Nwogwgwu, bisa zargin neman lalata da wata dalibar ‘yar shekara 17.

Kungiyar kare hakkin dan Adam mai suna Behind Bars Human Rights Foundation, reshen Jihar Abia, ce ta shigar da korafi zuwa ga hukumar gudanarwar jami’ar da kuma ofishin ‘yan sanda na Okpualangwa kan wannan zargi.

A cewar wata sanarwa daga jami’ar da ke dauke da kwanan watan 29 ga Mayu, 2025, Nwogwgwu ya samu dakatarwa nan take ba tare da kayyade lokaci ba, sannan za a gurfanar da shi gaban kwamitin ladabtar da ma’aikata na jami’ar domin gudanar da bincike.

Sanarwar ta kuma tabbatar wa jama’a cewa sakamakon jarrabawar jami’ar na hannun Sashen Rijista bayan amincewar Majalisar Jami’a, kuma duk wanda ke da matsala da sakamakonsa zai iya tunkarar sashen rijista domin warware matsalar.

A nasa bangaren, Daraktan Behind Bars Human Rights Foundation na Jihar Abia, Marvelous Ochiegbu, ya yaba wa jami’ar bisa saurin daukar mataki, tare da neman adalci da gaskiya wajen gudanar da binciken.

Ochiegbu ya nemi a ba kungiyar su damar shiga cikin tsari na binciken domin tabbatar da cewa ba a yi rikon sakainar kashi ba. Ya kuma bukaci a kare dalibar daga duk wata barazana ko ramuwar gayya.

More from this stream

Recomended