Wata gobara ga ƙone wata mata da ƴaƴanta uku ƙurmus a Kano

Al’ummar Agadasawa a jihar Kano sun shiga cikin mummunan yanayi bayan da wata gobara ta tashi tare da halaka wata mata da ‘ya’yanta uku.

Mummunan lamarin da ya jawo juyayin dubban jama’a a fadin jihar.

An ce lamarin ya faru ne da tsakar daren ranar Laraba a lokacin da marigayan ke barci.

Marigayiyar, Zainab, da ‘ya’yanta uku, Amatullahi, Amaturrahman, Safiyya, da Muhammad, iyalan wani dan kasuwan Kano ne mai suna Ado Muhammad Uba.

Wani dan uwansa mai suna Jazuli Jibril Aminu ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a lokacin da aka dawo da wutar lantarki, inda matar ta manta da kashe firjin da ta saka, wanda hakan ya yi sanadiyar fashewar silindar gas din.

A cewar Aminu, Zainab cikin takaici ta yi kokarin ceto ‘ya’yanta daga gobarar, amma kokarinta ya ci tura.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...