Hukumar ‘Yan Sandan Jihar Legas ta sallami ‘yan sanda hudu bisa zargin hannu a kisan wasu ‘yan kasuwa bakwai a yankin Owode-Onirin na jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Legas, Mista Olohundare Jimoh, ya tabbatar da wannan mataki yayin da yake ganawa da ‘yan jarida a Ikeja ranar Alhamis, inda ya ce bincike kan lamarin na ci gaba.
Kwamishinan ya bayyana cewa, “An kawo waɗannan ‘yan sandan daga Nasarawa ta hannun babban mai laifi da ake kira ‘Ariori’, wanda ake zargin yana da hannu sosai a kisan.”
Jimoh ya kara da cewa hukumar tana da nufin tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa, yana mai cewa binciken ya dogara da hujjojin kimiyya ciki har da rahotannin gwajin bindiga da na gawa.
“Ba za a boye wannan al’amari ba, kuma muna son jama’a da iyalan wadanda abin ya shafa su san cewa babu wanda zai hana mu tabbatar da adalci. Ba za mu yi kasa a gwiwa ba, kuma babu wanda zai tsorata mu. Duk wadanda ake zargi za a gurfanar da su a kotu,” in ji shi.
Kwamishinan ya jaddada cewa hukumar ‘Yan Sandan Najeriya na ci gaba da daukar nauyin tabbatar da doka da oda a fadin jihar, kuma babu wanda zai toshe hanyoyin shari’a yayin da bincike ke kusa kammala.
Ya ce an kammala kashi 98 cikin 100 na binciken, kuma hukumar zata ci gaba da daukar matakan kare ‘yan kasuwa da mazauna jihar.
Wasu ‘Yansandan Najeriya Guda Huɗu Sun Rasa Aikinsu Saboda K¡san ‘Yan Kasuwa Bakwai

