Wasu masu garkuwa da mutane sun faɗa hannun ƴan sanda a Kaduna

Rundunar yan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta sun kama wasu gawurtattun masu garkuwa da mutane su 4 da suka shahara  wajen yin garkuwa da mutane a yankin arewa maso yamma.

Bindiga  ƙirar AK-47 da kuma wata ƙaramar bindiga ƙirar gida aka gano daga wurin masu garkuwar.

A wata sanarwa da rundunar ƴan sandan jihar ta fitar mai magana da yawun rundunar ASP Mansir Hassan ya bayyana cewa a ranar 29 ga watan Mayu bisa dogaro da bayanan sirri da wani ɗan kasa nagari ya kwarmata musu haɗin gwiwar sintirin jami’an tsaro daga ofishin ƴan sanda na Saminaka da kuma ƙungiyar mafarauta dake ƙaramar hukumar Lere suka samu nasarar kama masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu su uku.

Mai magana da yawun rundunar ya ce waɗanda aka kama sun haɗa da Isah Baffa Rabo mai shekaru 30 daga ƙauyen Maibindiga a ƙaramar hukumar Lere wanda yake da hannu a yin garkuwa da mutane a ƙananan hukumomin Zangon Kataf da Kachia dake jihar, Jafaru Saleh mai shekaru 30 da kuma Umar Musa mai shekaru 24 dukkansu sun fito daga ƙauyen Durimi dake Lere.

Mutanen sun amsa laifin yin garkuwa da mutane da kuma satar shanu biyu da suka sayarwa da wani Idris Abubakar da shima ya faɗa hannun jami’an tsaro.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...