
Wani yaro dan shekara 13 mai suna Dayyabu Salisu ya nutse a ruwa lokacin da yake wanka a wani kududdufi dake kauyen Yankatsari a karamar hukumar Dawakin Kudu dake Kano.
Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya fadawa kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN cewa lamarin yafaru ne a ranar Laraba da safe lokacin da marigayin yaje wanka.
Muhammad ya ce” mun samu kiran kai daukin gaggawa daga wani mutum mai suna Mallam Aminu Sani da misalin karfe 10:25 na safe inda ya ce anga gangar jikin Salisu na yawo akan ruwa kududdufi.
“Muna samun kiran mun tura jami’an mu dake aikin ceto zuwa wurin da misalin karfe 10:55.
“Mun samu Salisu a mace kuma daga bisani an mikawa mahaifinsa,Mallam Salisu Abdullahi gawarsa,” ya ce.