Wani ya kashe ƴar da ya haifa saboda namiji ya fi so a haifa masa

Wani lamari mai matukar tayar da hankali da ban tausayi ya faru yayin da hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wani matashi dan shekara 28 mai suna Misbahu Salisu bisa zarginsa da sanya wa jaririyarsa guba.

An bayyana cewa, wannan mummunan lamari ya faru ne saboda fifikon da mutumin ya yi wa ɗa namiji.

Lamarin ya faru ne a garin Doka Baici da ke karamar hukumar Tofa, lamarin da ya jefa al’umma cikin fargaba.

A cewar wata sanarwa da mataimakin babban kwamandan ayyuka na hukumar Hisbah ta jihar Kano, Mujahid Aminudeen, ya fitar, wanda ake zargin ya amince da aikata wannan mummunan aiki.

Bugu da kari, ya ba wa mahaifiyar jaririyar mai suna Sa’ade miyagun kwayoyi da wani kofin shayi da aka sa maganin barci kafin ya aikata laifin.

An bayyana wadannan bayanai masu ban tsoro yayin binciken hukumar.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...