[ad_1]
Rundunar Æ´ansandan jihar Ondo ta bayyana cewa mutumin da ta kama wanda ake zargi da yin garkuwa da mutane na cigaba da sharara bacci kwanaki shida bayan da aka kama shi.
An kama mutumin da ake zargin a ranar Lahadi lokacin da shi da sauran abokan ta’addancinsa suka yi Æ™oÆ™arin yin garkuwa da wata mata dake da shagon sayar da magunguna a Owo dake jihar Ondo.
Ance mutumin ya fita daga hayyacinsa lokacin da suke tsaka da shirin yin garkuwa da matar.
Femi Joseph, mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Ondo ya ce har ya zuwa yanzu Æ´ansanda sun gaza tatsar wasu bayanai masu muhimmanci a gurinsa.
Joseph ya ce litita ya tabbatar da cewa ya daddaki kwayar Tramadol mai yawa shiyasa yake ta sharara bacci.
Ya kara da cewa an samu 400mg na Tramadol aljihunsa lokacin da aka kama shi.
[ad_2]