Mutane da dama ne suka makale a kasan É“araguzan wani gini da ya ruguzo a yankin Sabon Lugbe dake birnin tarayya Abuja.
Wasu bayanai sun bayyana cewa ginin ya ruguzo ne da yammacin ranar Asabar.
Wasu fefayen bidiyo da aka wallafa a soshiyal midiya sun nuna yadda mutane suke aikin ceton mutanen da abun ya rutsa da su.
“Mutane suna Æ™asan É“araguzai gini ne da ake kan aikinsa.”
“Muna kira ga gwamnati da hukumomin da abun ya shafa da su zo su ceto mutanennda suka maÆ™ale a cikin É“araguzan ginin,”a cewar wani dake magana da manema labarai a wurin.
Kawo yanzu dai babu wata sanarwa daga hukumomi kan yawan mutanen da abun ya rutsa da su.
Rushewar ginin na zuwa ne Æ´an kwanaki kaÉ—an bayan da wani ya ruguzo a jihar Lagos.