[ad_1]
Wani dan Najeriya dake ƙasar Afirka ta Kudu,Okolie Olileanyi Paul ya rasa ransa a hannun danuwansa dan Najeriya.
Hakan na zuwa ne kusan makonni uku bayan da wani dan Najeriya, Lawrence Nwarienne ya harbe wani dan Najeriya,Chibuzor Nwanko mai shekaru 42.
Ƙungiyar yan Najeriya dake zaune a kasar Afirka ta Kudu a wata sanarwa da jami’in yada labaran kungiyar,Cif Iyke Odefa,ya fitar ya ce, Paul mai shekaru 28 a duniya, ya fito ne daga karamar hukumar AAwgu ta Jihar Enugu ana zargin ya mutu sakamakon caka masa wuka da wani mai suna, Donald Modi ya yi, wanda ya fito daga karamar hukumar Ika maso gabas dake jihar Delta.
Oyedafa ya ce an cakawa marigayin wuka ne sakamakon ce-ce kuce har ta kai su ga yin faÉ—a.
[ad_2]