Mutumin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya turawa majalisar dattawa domin tantancewa a matsayin minista ya yanke jiki ya faɗi a majalisa.
Balarabe Abbas Lawal shi ne aka zaba ya zama minista daga jihar Kaduna bayan da majalisar dattawa taki amincewa da Elrufai.
Abbas ya fadi ne dai-dai lokacin da ya kammala jawabi akan tarihinsa da karatun da yayi.
Shugaban majalisar dattawan, Godswill Akpabio ya yi gaggawar kiran likita domin su duba halin da yake ciki.