[ad_1]
Masu garkuwa da Talatu, matar Hosea Akuchi wani fasto da ƴanbindiga suka kashe sun bukaci a biya su miliyan ₦5 kafin su sake ta.
An sace matar ne bayan da aka kashe mijinta dai-dai lokacin da ya yi wa masu garkuwar turjiya a gidansu dake Guguwa a karamar hukumar Igabi.
Wata majiya dake cocin ta bayyana cewa masu garkuwa sun tuntubi iyalan faston domin bayyana buƙatar tasu.
“Masu garkuwar sun kira yau inda suka ce suna bukatar mu biya su miliyan ₦5 kafin su sako mana ita.
[ad_2]