Uba Sani ya bayar da umarnin yin bincike kan harin soja da ya kashe mutane 30

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba sani ya bayar da umarnin bincike kan harin jirgin sama da ya kashe mutane da dama a ƙauyen Tudun Birni dake ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

A wata sanarwa ranar Litinin ya ce gwamnati ta kudirin aniyar ganin cewa hari makamancin wannan bai sake faruwa ba ana gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa an jefa bam ne kan mutanen ƙauyen lokacin da suke gudanar da taron Maulidi.

Tun da farko rundunar sojan Najeriya ta amsa alhakin kai harin inda ta ce an kai shi ne a bisa kuskure.

Gwamnan ya ce tuni ya tura jami’an gwamnati ya zuwa Æ™auyen domin zaÆ™ulowa tare da ceto waÉ—anda abun ya shafa.

“Na kuma bayar da umarnin É—auke waÉ—anda suka jikkata ya zuwa Asibitin Koyarwa na Barau Dikko domin samun kulawar gaggawa. Gwamnati ta dauki nauyin kuÉ—in maganinsu dana É—awainiyarsu.” a cewar sanarwar.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...