Tunisia: Za a daidaita rabon gado tsakanin maza da mata

[ad_1]

Shugaba Essebsi

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Shugaba Essebsi ya ce Tunisia kasa ce mai sassaucin ra’ayi.

Shugaban Tunisia zai bayyana wata sabuwar doka da za ta daidaita rabon gado tsakanin maza da mata.

Shugaba Beji Caid Essebsi ya ce zai gabatar da kudurin dokar ga Majalisar dokokin kasar.

A adinin musulunci maza sun fi mata samun kaso mai yawa , sai dai shugaba Essebsi ya nanata cewa Tunisia kasa ce mai sassaucin ra’ayi.

Ana sa ran zai sanar da kudurin daidaita rabon gado tsakanin maza da mata a ranar mata ta duniya .

Haka kuma ana ganin shugaban zai sanar da kudurin kare hakkin yan luwadi da madugo, sai dai ya ce zai kafa wani kwamiti da zai yi nazari kan shirin nasa kafin ya wallafa shi domin kaucewa fushin yan kasar, ko kuma a bayyana shi a matsayin wanda ya yi ridda.

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...