Tsohon Ministan Sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Pantami, ya bayyana alhininsa kan ibtila’in da ya afkawa wasu ‘yan kasuwa a kasuwar wayoyi ta Pantami, inda gobara ta kona musu shaguna da kayayyaki.
Farfesa Pantami ya bayyana hakan ne cikin wata wallafa da ya yi a dandalin Facebook da daddare ranar jiya, inda ya ce yana mika jajensa ga ‘yan uwan da lamarin ya shafa.
“Ina mika sakon jaje ga ‘yan’uwanmu ‘yan kasuwar wayoyi (Smartphones) da ke Pantami wadanda gobara ta shafa ta kona musu shaguna,” in ji shi.
Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da Ya mayar musu da abin da suka rasa da mafi alheri, tare da bukatar gwamnati da sauran masu hannu da shuni da su tallafa musu domin rage musu radadin wannan bala’i.
“A rokonmu, Allah Ya mayar musu da mafi alheri sannan kuma Ya bawa gwamnati da sauran masu rufin asiri daman tallafawa gare su. Allah Ya kiyaye faruwar haka nan gaba,” in ji Farfesa Pantami.
A halin yanzu, har yanzu ba a bayyana adadin da wannan gobara ta shafa ba, sai dai rahotanni na nuna cewa shaguna da dama sun kone kurmus.
Tsohon Minista Isa Ali Pantami Ya Aike Da Sakon Jaje Ga ‘Yan Kasuwar Waya Na Pantami Da Gobara Ta Shafa
