Trump Ya Ce Ya Kamata Ya  Zama Cikin Masu Zaɓen Sabon Jagoran Addinin Iran

Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa ya kamata ya kasance cikin waɗanda za su zaɓi sabon jagoran addinin Iran.

Trump ya yi wannan bayani ne a wata tattaunawa da kafar labarai ta Axios, inda ya ce yana kyautata zaton cewa jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta zaɓi ɗan marigayi Ayatollah Khamna’i, wato Mojtaba Ali Khamna’i, a matsayin sabon jagora. Sai dai Trump ya ce lamari ne da ba zai taɓa amincewa da shi ba.

A halin yanzu, cibiyar ƙwararru da ke da alhakin naɗa sabon jagoran ba ta bayyana wanda zai gaji Ayatollah Ali Khamna’i ba. Marigayin ya rasu ne bayan harin da ake zargin Amurka da Isra’ila sun kai a birnin Tehran ranar Asabar da ta gabata.

Hukumomi ba su sanar da ranar jana’izar marigayin ba, bayan ɗage ta a farkon makon nan saboda fargabar turmutsutsu, kasancewar ana tsammanin tururuwa mai yawa za ta halarci wajen binne shi.

More from this stream

Recomended