Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa na ci gaba da yin “ƙoƙari” a yaƙin da take yi da Iran.
Trump ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai a jihar Florida. Ya ce a cikin kwanaki uku kacal, sojojin Amurka sun nutsar da jiragen ruwan Iran guda 42 a cikin teku.
Shugaban ya kuma bayyana cewa zai kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan sojojin Amurka da suka mutu a yaƙin.
Ya ce sojojin da suka mutu sun zama “manyan jaruman ƙasarmu”, inda ya ƙara da cewa za a dawo da gawawwakinsu daga Iran cikin wani yanayi na daban.
Trump ya kuma jaddada cewa Amurka za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin mutuwar sojojinta ta “taƙaita”.
Trump Ya Ce Amurka Na Yin Ƙoƙari A Yaƙin Iran

