Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa yana son rage hare-haren da ake kai wa Iran, inda ya alƙawarta cewa yaƙin zai kawo ƙarshe cikin mako biyu zuwa uku masu zuwa, ko da an cimma yarjejeniya ko ba a cimma ba.
Ya ce yanzu Iran tana da sababbin shugabanni waɗanda “suka fi sauƙin samu, ba masu tsattsauran ra’ayi ba kuma wadanda suka fi magabatansu hankali.”
Trump ya kara da cewa gwamnatin Amurka ta cimma burinta, duk da cewa ba ta samu damar kwace mashigar Hormuz daga hannun Iran ba. Wannan yanayi ya sa yuwuwar ci gaba da karancin mai da farashin danyen man ya tashi a yau Laraba.
Sai dai ya yi nuni cewa nan gaba kadan farashin zai sauka. A yau, zai gabatar da jawabi ga al’ummar Amurka ta talabijin.
Trump Ya Alƙawarta Kawo Karshen Yaƙin Iran

