Tinubu zai wuce Paris daga London

Shugaba Bola Tinubu na shirin zuwa birnin Paris na kasar Faransa daga birnin Landan na kasar Birtaniya, a kowane lokaci daga yanzu don wani ‘muhimmiyar hulda’.

Wani makusancin siyasa na Tinubu, Ibrahim Kabir Masari ne ya bayyana hakan a yammacin ranar Juma’a.

Rahotanni sun ruwaito cewa, Shugaba Tinubu ya tafi Landan ne a ranar 2 ga Oktoba, 2024, domin hutun makonni biyu.

Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ta ce “hutun aiki” wani bangare ne na hutunsa na shekara. 

An kuma ce shugaban zai dawo Najeriya bayan kammala hutun.

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja yau zuwa kasar Ingila domin fara hutun makonni biyu, na hutun shekara.

Sanarwar ta ce “zai dawo kasar bayan hutun ya kare.”

More News

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

Magoya bayan jam’iyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta É—auki hanyar warware rikicin jam’iyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban Æ™ungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...