
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya naɗa, Ismail Abba Yusuf a matsayin shugaban Hukumar Aikin Hajji ta Kasa NAHCON.
An sanar da naɗin nasa ne a wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba ta bakin mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga.
Sanarwa ta ce nadin zai fara aiki ne bayan sahalewar majalisar dattawa kamar yadda sashi na 3(2) na dokar NAHCON ta 2026 ya tanada.
” Shugaban kasa Tinubu ya aika da wasika ga shugaban majalisar dattawa, Godswil Akpabio inda ya nemi a gaggauta tabbatar da Ambasada Yusuf domin ya maye gurbin Farfesa Abdullahi Usman Saleh wanda ya yi murabus a wannan satin bayan ya shafe watanni 14 a muƙamin,” a cewar sanarwar.
An naɗa Yusuf ne biyo bayan murabus din da shugaban hukumar NAHCON, Abdullahi Usman ya yi a ranar Litinin.

