Tinubu ya naɗa sabuwar shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya 

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince da naɗin, Misis  Didi Esther Walson-Jack,OON   a matsayin sabuwar shugabar ma’aikata ta Najeriya.

A cewar mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale naɗin nata zai fara aiki ne daga ranar 14 ga watan Agusta.

An naɗ Misis Walson-Jack  matsayin babbar sakatariya a shekarar 2017 inda kuma tayi aiki a ma’aikatu da dama-dama.

Sabuwar shugabar ma’aikatan za ta karɓi aiki ne daga shugabar ma’aikatan ta yanzu Dr. Folasade Yemi-Esan, CFR wacce za ta yi ritaya ranar 13 ga watan Agusta.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]