Tinubu ya miƙa tuta ga ƴan takarar APC a zaɓukan gwamna na jihohin Kogi, Bayelsa da Imo

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya miƙa tuta ga yan takarar gwamna a jam’iyar APC a zaɓen da za ayi a jihohin Bayelsa, Kogi da kuma Imo.

A ranar 11 ga watan Nuwamba ne aka shirya gudanar da zaɓukan gwamna a jihohin uku.

Ƴan takarar na jam’iyar APC sun haɗa da Hope Uzodimma wanda yake neman a sake zaɓensa a matsayin gwamnan jihar Imo, sai Timpre Sylva a jihar Bayelsa da kuma Usman Ododo wanda yake neman a zaɓe shi a matsayin gwamnan Kogi.

Tinubu ya yi kira da a gudanar da sahihin zaɓe ba tare da tahin hankali ba.

A yan kwanakin nan hukumar zaɓe mai zaman kanta ƙasa INEC ta nuna damuwarta kan yadda ake yawan samun rikice-rikice da ya shafi ƴan takara da kuma jam’iyunsu a jihohin uku

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...