Tinubu ya isa Amurka don halartar taron MDD

A ranar Lahadin ne shugaba Bola Tinubu ya isa birnin New York domin halartar manyan tarukan babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78.

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa Mista Tinubu ya isa filin jirgin sama na JF Kennedy da ke birnin New York da misalin karfe 6:45 na yamma agogon kasar.

Shugaban kasar dai yana jagorantar tawagar Najeriya ne domin halartar taron da aka shirya gudanarwa tsakanin ranakun 18 zuwa 26 ga watan Satumba wanda shi ne karon farko da zai fara aiki a matsayinsa na shugaban kasar Najeriya.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...