Tinubu ya isa Amurka don halartar taron MDD

A ranar Lahadin ne shugaba Bola Tinubu ya isa birnin New York domin halartar manyan tarukan babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78.

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa Mista Tinubu ya isa filin jirgin sama na JF Kennedy da ke birnin New York da misalin karfe 6:45 na yamma agogon kasar.

Shugaban kasar dai yana jagorantar tawagar Najeriya ne domin halartar taron da aka shirya gudanarwa tsakanin ranakun 18 zuwa 26 ga watan Satumba wanda shi ne karon farko da zai fara aiki a matsayinsa na shugaban kasar Najeriya.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin É—aliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da É—aliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...