Tinubu ya gana da TY Danjuma

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a ranar Asabar ya gana da tsohon ministan tsaro, Janaral Theopillus Yakubu Danjuma a fadar Aso Rock dake Abuja.

Fadar shugaban kasar ce ta sanar da ganawar a cikin wasu hotuna da ta fitar dauke da gajeren sako.

Sako ya bayyana cewa ” Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya karbi bakuncin, Janaral Theopillus Yakubu Danjuma mai ritaya a fadar shugaban kasa dake Abuja ranar Asabar 28 ga watan Fabrairu 2026.”

Har kawo yanzu ba a bayyana dalilin ganawar ta su.

More from this stream

Recomended