Tinubu Ya Gana Da Sultan na Sokoto da Shugabannin Addini a Fadar Shugaban Kasa

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya karbi bakuncin Sultan na Sokoto da Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya, Alhaji Sa’ad Abubakar III, tare da wasu shugabannin gargajiya da na addini a Fadar Shugaban Kasa a Abuja ranar Litinin.

Taron ya zo ne a matsayin iftar na haɗin addinai, wanda aka shirya musamman domin shugabannin addini da na gargajiya a Najeriya.

Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ceci ƙasar daga fadawa cikin matsin tattalin arziki, kuma yanzu tana mai da hankali kan bunkasa fannonin ilimi, lafiya da noma.

Ya ce, “A kalla, wannan gwamnati ta ceci Najeriya daga fadawa cikin ƙunci na tattalin arziki. Yanzu muna mai da hankali kan lafiya, noma da ilimi.”

More from this stream

Recomended