Tinubu ya gana da Badaru da Ganduje

A ranar Talata ne shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu  ya gana da tsohon shugaban jam’iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da kuma tsohon ministan tsaro, Badaru Abubakar.

Shugaban ƙasar ya gana da mutanen biyu a lokuta mabanbanta a fadar shugaban ƙasa dake Abuja.

Kawo yanzu dai babu wanda ya san abun da ganawar tasu ta mayar da hankali kuma dukkan su sun gaza yiwa yan jaridu dake fadar shugaban kasa jawabi bayan fitowarsu daga ganawar.

Wasu masana na ganin ganawa da Ganduje da shugaban ƙasar ya yi bata rasa nasaba da halin da ake ciki a siyasar jihar Kano inda jam’iyar adawa ta ADC ke samun ƙarin goyon baya tun bayan da jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso ya koma jam’iyyar.

More from this stream

Recomended