
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo gida Najeriya bayan ziyarar aiki da ya kai kasar Turkiyya.
Jirgin da ya dauko shugaban kasar ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja da misalin karfe 08:55 na daren ranar Asabar.
Fadar shugaban kasa ta tabbatar da dawowar Tinubu a cikin wani gajeren sako da ta aikewa da yan jaridar dake fadar shugaban kasa.
Tinubu ya fara ziyarar aikin ne a ranar Talata.
A yayin ziyarar Tinubu ya gana da shugaban kasar Turkiyya, Recep Tayyib Erdogan.
Ganawar ta mayar da hankali kan karfafa dangantaka a tsakanin ƙasashen biyu a fannoni da dama.

