Tinubu ya dawo daga kasar Turkiyya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo gida Najeriya bayan ziyarar aiki da ya kai kasar Turkiyya.

Jirgin da ya dauko shugaban kasar ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja da misalin karfe 08:55 na daren ranar Asabar.

Fadar shugaban kasa ta tabbatar da dawowar Tinubu a cikin wani gajeren sako da ta aikewa da yan jaridar dake fadar shugaban kasa.

Tinubu ya fara ziyarar aikin ne a ranar Talata.

A yayin ziyarar Tinubu ya gana da shugaban kasar Turkiyya, Recep Tayyib Erdogan.

Ganawar ta mayar da hankali kan karfafa dangantaka a tsakanin ƙasashen biyu a fannoni da dama.

More from this stream

Recomended