Tinubu ya dakatar da gwamnan babban Najeriya Emefiele

Shugaba Bola Tinubu ya amince da dakatar da Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya.

Daraktan ofishin yada labarai na sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey ne ya bayyana hakan a cikin wata ‘yar gajeruwar sanarwa a daren Juma’a.

Ya bayyana cewa yana mayar da martani ne ga wani bincike da ofishinsa ke gudanarwa da kuma sake fasalin fannin hada-hadar kudi da ke tafe.

An umurci Emefiele da ya gaggauta mika ragamar tafiyar da harkokin ofishinsa ga mataimakin gwamna (Operations Directorate), wanda zai yi wannan aiki har sai an kammala bincike da sauye-sauye.

More News

Hukumar NDLEA ta lalata sama da tan 300 na miyagun kwayoyi da aka kama a Legas da Ogun

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta yi nasarar lalata kilogiram 304,436 da lita 40,042 na haramtattun abubuwa da...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...