Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da aikin manyan tituna guda shida a sassa daban-daban na Najeriya.
Haka kuma ya amince da rusa gadar Carter da ke Legas tare da sake fasalin wata sabuwar gada a wurin.
Ministan Ayyuka, Dave Umahi, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba. Ya ce daga cikin ayyukan da aka amince da su akwai titin Suleja zuwa Minna, wanda tun da farko aka bai wa kamfanin Salini Construction, amma aka soke kwangilar sakamakon rashin gamsasshen aiki.
Umahi ya ce kilomita 10 kacal aka kammala kafin a dakatar da aikin.
Gwamnatin tarayya ta yanke shawarar kammala sauran kilomita 71 na titin mai layi biyu. An bai wa kamfanin China Geo-Engineering Corporation (CGC) ɓangare ɗaya kan kuɗi naira biliyan 91. Ya ƙara da cewa Hukumar BPP ta amince da ɓangaren na biyu.
Tinubu Ya Amince Da Manyan Ayyukan Tituna Shida A Faɗin Najeriya

