Shugaba Bola Tinubu ya amince da karin Naira 10,000 ga ma’aikata na tsawon watanni shida.
Hakan ya biyo bayan wani taro da jami’an gwamnatin tarayya suka yi da shugabannin kwadago a ranar Lahadi domin dakile yajin aikin da ke kunno kai a fadin kasar.
A taron da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila ya jagoranta, an amince da cewa za a ba wa dukkan ma’aikata naira 25,000 da shugaban kasa ya yi alkawarin ba wa kananan ma’aikata na tsawon watanni shida.
Sai dai rahotanni sun ce shugabannin jam’iyyar ƙwadago sun yi watsi da tayin tare da neman karin wasu.
Bayan haka ne fadar shugaban kasar ta fitar da sanarwar karin 10,000.