Tinubu ya amince da ƙarin N10,000 ga ƙananan ma’aikata bayan karin N25,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da karin Naira 10,000 ga ma’aikata na tsawon watanni shida.

Hakan ya biyo bayan wani taro da jami’an gwamnatin tarayya suka yi da shugabannin kwadago a ranar Lahadi domin dakile yajin aikin da ke kunno kai a fadin kasar.

A taron da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila ya jagoranta, an amince da cewa za a ba wa dukkan ma’aikata naira 25,000 da shugaban kasa ya yi alkawarin ba wa kananan ma’aikata na tsawon watanni shida.

Sai dai rahotanni sun ce shugabannin jam’iyyar ƙwadago sun yi watsi da tayin tare da neman karin wasu.

Bayan haka ne fadar shugaban kasar ta fitar da sanarwar karin 10,000.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...