Tinubu ya aika wa majalisa sunayen wasu da zai naɗa a matsayin ministoci

Shugaba Bola Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta amince da wasu mutane uku da zai nada a matsayin Ministocin Tarayyar Najeriya.

Bukatun Mista Tinubu na kunshe ne a cikin wata wasika da ya aike wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da aka karanta a zauren majalisa ranar Talata.

Mista Tinubu a cikin wasikar ya ce: “A bisa bin tanadin sashe na 147, karamin sashe na 2 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya 1999 da aka yi wa kwaskwarima.

“Na yi farin cikin mika wa majalisar dattawa mutane uku da aka tantance domin tabbatarwar da majalisar dattawa.

“Dr Jamila Biu Ibrahim, Balarabe Abass Lawal, da Ayodele Olawale domin tabbatar da su a matsayin ministocin Tarayyar Najeriya.”

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...