Shugaba Bola Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta amince da wasu mutane uku da zai nada a matsayin Ministocin Tarayyar Najeriya.
Bukatun Mista Tinubu na kunshe ne a cikin wata wasika da ya aike wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da aka karanta a zauren majalisa ranar Talata.
Mista Tinubu a cikin wasikar ya ce: “A bisa bin tanadin sashe na 147, karamin sashe na 2 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya 1999 da aka yi wa kwaskwarima.
“Na yi farin cikin mika wa majalisar dattawa mutane uku da aka tantance domin tabbatarwar da majalisar dattawa.
“Dr Jamila Biu Ibrahim, Balarabe Abass Lawal, da Ayodele Olawale domin tabbatar da su a matsayin ministocin Tarayyar Najeriya.”