
Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar Juma’a ya ƙaddamar da wasu ayyukan raya kasa a jihar Bayelsa a wata ziyarar aiki da ya kai jihar.
Ɗaya daga cikin manyan ayyukan da shugaban kasar ya ƙaddamar shi ne aikin sabuwar tashar samar da wutar lantarki daga iskar gas mai karfin megawatts 60 da gwamnatin jihar ta samar a garin Elebele dake karamar hukumar Ogbia ta jihar.
Shugaban ya kuma ƙaddamar da wasu ayyukan gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Douye Diri ta samar ciki har da gadar Angiama-Oporoma mai tsawon mita 630.
Sauran ayyukan da shugaban ƙasar ya ƙaddamar sun haɗa da titin Sagbama/Ekeremor da kuma titi mai tsawon kilomita 2.9 da aka mai da shi hannu biyu a Yenogoa babban birnin jihar.
Ba kamar a birnin Lagos ba da shugaban ƙasar ya wakilta shugaban majalisar wakilai ta tarayya, Godswil Akpabio domin ya wakilce shi a yayin kaddamar da wasu ayyuka. A wannan karon shugaban ne yagoranci bikin.
Da yake magana a wurin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar Tinubu ya yabawa gwamna Diri kan yadda ya samar da tashar samar da wutar lantarkin mai zaman kanta.
Shugaban kasar ya ce yan jihar Bayelsa sun cancancin ganin mulki dake samar da cigaba da kuma inganta rayuwar al’umma.

