Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naɗa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai naɗa  a matsayin ministoci a gwamnatinsa.

Buƙatar da Tinubu ya aikewa majalisar na ƙunshe ne cikin wata takarda da shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya karanta a zaman majalisar na ranar Alhamis.

A ranar Laraba ne dai shugaban ƙasar ya sanar da sallamar wasu ministoci daga muƙaminsu tare da sanar da maye gurbinsu da wasu.

Wannan ne karon farko da shugaban ke yiwa majalisar ministocinsa garambawul tun bayan da  aka rantsar da su shekarar da ta wuce.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...