Taron G7: ‘Rikicin Libya na kara tsananta matsalar tsaro a yankin Sahel’

Akwai sojojin kasashen duniya da ke yaki da ta'addanci a yankin Sahel

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Burkina Faso Marc Kabore ya bukaci shugabannin kasashen duniya su mayar da hankali wajen kawo karshen rikicin da ake fama da shi a Libya kafin a iya kakkabe ta’addancin da ke bazuwa a fadin Sahel.

Shugaban ya fadi hakan ne a wani jawabi da ya gabatar a taron kolin manyan kasashe bakwai masu ci gaban masana’antu a Biarritz tare da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron.

Mista Kaboré ya yi kira da a samar da isassun kudade ga rundunar yaki da ta’addanci da ke aiki a yankin Sahel mai lakabin G- five.

Shi dai shugaba Kabore, wanda a makon jiya aka kashe sojojin kasarsa 24 tare da jikkata wasu guda 7 a wani harin ‘yan tayar da kayar baya, ya bayyana ta’addanci amatsayin wata masifa da ke bazuwa a Afirka.

Ya ce “Masifa ce da ke yaduwa, kuma mun yi kiyasin cewa sai dukkanin abokan kawance sun hadu domin lalubo mafita ga matsalar tsaro a Libya.”

Ya kara da cewa sai kasashen duniya sun zuba jari wajen samar da ayyukan raya kasa da ayyukan soja, kafin zaman lafiya ya tabbata a yakin Sahel.

A nata jawabin a wurin taron na G7, shugabar Jamus Angela Merkel ta ce al’amura na ci gaba da tabarbarewa a Sahel.

Ta ce abin da ke faruwa a Afirka abin damuwa ne, saboda haka akwai bukatar al’ummomin kasashen duniya su hanzarta tashi tsaye domin ganin kungiyoyin ‘yan ta’adda ba su samu wurin zama ba a can.

Ta ce “A yakin da muke yi, ba mu kai gabar da za mu ce sha’anin tsaro ya inganata ba”.

More from this stream

Recomended