Wani bala’i ya afku a ranar Lahadin a kusa da titin Baban Gwari da ke kan titin Katsina a jihar Kano inda wasu mutane biyu suka rasa rayukansu bayan da suka makale a cikin wata tankar ruwa.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Saminu Abdullahi ya fitar ranar Lahadi.
Abdullahi ya ce yayin da suke cikin tankin, wadanda abin ya shafa sun fita daga hayyacinsu zato ba tsammani sakamakon shakewar da suka yi.
Ya bayyana cewa wani direban babbar mota da ya isa wurin, shi ne ya kawo labarin a lokacin da aka neme su ta wayar tarho ba a dame su ba.